Tsakure:
Wannan takarda ta gudanar da nazari ne kan irin gudummuwar da harshen Hausa yake bayarwa wajen ƙulla sulhu da samar da tsaro a Jihar Katsina. Manufar wannan takarda ita ce, nazarin irin rawar da harshen Hausa yake takawa wajen sasanta tsakanin al’umma da masu garkuwa da mutane da jami’an tsaro da shuwagabannin al’umma. An yi amfani da nau’in bincike na bayani. An tattauna da masu ruwa da tsaki da kuma nazarin ayyukan masana. An yi amfani da ra’in sulhu (Conflict Resolution Theory), a wannan bincike. An gano cewa, harshen Hausa yana taka gaggarumar rawa wajen ƙulla sulhu da sasanci a tsakanin al’umma. An gano cewa, amfani da harshen, yana ceton ɗimbin rayukan mutane daga salwanta fiye da yin amfani da ƙarfi, ko bindiga. An bayar da shawara a kan yadda za a ƙarfafa horo ga jami’an tsaro dangane da dabarun iya sadarwa da harshen Hausa, domin a magance matsalar tsaro. Hukuma ta riƙa sanya shuwagabannin al’umma na gargajiya da malamai a cikin tsarin tsaro. Yin hakan zai taimaka wajen gano bakin zaren wuraren da matsala take.
Muhimman Kalmomi: Harshe, Sulhu, Garkuwa.
DOI: 10.36349/djhs.2026.v04i01.003
author/Adam Magaji
journal/Dundaye JOHS, July 2026
